Sunday, 3 December 2017
News updates:Atiku Abubakar ya koma PDP
Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Alhaji Atiku Abubakar
ya koma jam'iyyar adawa ta PDP.
Dan siyasar ya bayyana hakan ne ta shafinsa na Facebook
ranar Lahadi.
Sai dai bai fito fili ya bayyana anniyarsa ta sake neman
shugabancin kasar a babban zaben kasar na shekarar 2019.
Ya ce ya koma jam'iyyar ne saboda matsalolin da suka sa ya
fice daga PDP a shekarar 2014 "an warware su yanzu."
Har ila yau ya ce jam'iyyar APC ta "kasa cika alkawurran da ta
yi wa al'ummar kasar musamman matasa."
baya dai Atiku Abubakar ya sha sauya jam'iyyun siyasa.
Kuma wannan ne karo na biyu da dan siyasar yake koma wa
jam'iyyar PDP.
Atiku Abubakar ya kasance mataimakin shugaban Najeriya ne
tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007.
A shekarar 2007 ne ya fara tsakayawa takarar shugabancin
Najeriya ne a karkashin jam'iyyar AC.
Hakazalika ya sake neman takarar a shekarar 2011, amma bai
samu tikitin jam'iyyarsa ta PDP ba.
Atiku Abubakar ya kara neman tsayawa a shekarar 2014, inda a
nan ma bai samu tikitin shugabanci ba a karkashin jam'iyyar
APC.
Domin samun sauran labarai kadanna Rubutunnan mai kala
Domin samun labarai gameda harkar ilimi kadannaRubutunnan mai kala
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment