Friday, 8 December 2017

Nigeria: An yankewa wasu mutane biyu masu yima yara fyade daurin rai dai rai a Bauchi


Wata babbar kotu a jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin
Najeriya ta yankewa wasu mutum biyu hukuncin daurin rai da
rai a gidan yari bayan samun su da laifin aikata fyade.

Kotun ta samu mutunen ne da laifin yi wa wata mace mai
shekara 40 fyade tare da kwakule mata ido.
Lamarin dai ya faru ne a garin Dass a shekarar 2014.
An shafe shekara biyu ana tafka shari'ar inda alkalin kotun ta
bayyana mutanen biyu a matsayin marasa imani da ya ce bai
kamata suna cudanya da al'umma ba.
Jama'a da dama dai sun yi marhabin da hukuncin da suka ce
zai zama darasi ga wasu da ke aikata fyade.
Matsalar aikata fyade dai matsala ce da ta zama ruwa dare a
Najeriya, sai dai ba kasafai ake hukunta wadanda suka aikata
laifin ba.
Kungiyoyin fararen hula sun sha gudanar da zanga-zanga kan
yadda al'umma a Najeriyar ke yin wasa-rai-rai da karuwar fyade a kasar.


Uploaded by abdulazeez alkasim Umar:

No comments:

Post a Comment