wani magidanci ya shiga hannun --hukuma bayan yayi lalata da
diyar sa bisa ga umarnin bokaye
An gurfanar da wani magidanci Bashiru Adeyanju a gaban
kotun majistere dake Ado-ekiti a jihar Ekiti bayan ya amince
cewa yayi lalata da diyar shi mai shekaru 17 bisa ga umarnin
bokaye domin ya samu arziki.
Bisa ga rahoton Tribune , Adeyanju ya amsa laifi cewa yayi
lalata da diyar kusan so 9 kana bokayen suma sunyi farna da
ita duk cikin tsarin neman kudi ta hanyar tsubbu.
Adeyanju wanda yace neman arziki yasa yayi lalata da diyar sa
kuma bai ji dadi ba ganin cewa shi kadai aka gurfanar gaban
ko yayin da bokayen suka tsere.
“Mu uku muka aikata laifi, amma nayi mamaki da na gana ni
kadai yan sanda suka gurfanar a gaban kotu” inji adeyanju.
Shugaban kotun Mrs Dolapo Akosile ta tabbatyar mai cewa
za’a gabatar da saura abokan aikin shi.
“Kada ka damu, za’a kawo saura gaban kotu”.
A bisa ga labarin Adeyanju, akwai wata farar kyallen hankicif
da yake shafar farjin diyar duk lokacin da ya sadu da ita kamar
yanda bokayen suka umarce shi, duk da cewa ya aikata haka
lokaci da dama shidai wannan magidancin bai cinma burinsa
na samun arziki.
Jami’in dan sanda da ta gurfanar da shi Sergeant Monica
Ikebuilo tace wanda ake tuhuma ya aikata laifi da ya sabawa
kundin tsarin mulkin jihar kuma ta roki kotu da a daga karar
har zuwa lokacin da hukumar dake yanke hukunci ta bada
shawara akan laifin.
Shugaban kotu ya bada umarni na a cigaba da rikon mai laifin
a gidan yari har zuwa ranar 12 ga watan Octoba bayan anji
shawarar hukumar zata bada.
Domin samun labarai kadanna WANNAN Bulan rubutu.
Monday, 13 November 2017
Ya kashe mahaifiyar sa kan zargin kashe diyar sa ta hanyar tsibbu
Magidancin ya kashe mahaifiyar sa mai shekari 100 tare da
taimakon mahaifin shi bisa ga zargin kashe diyar shi ta hanyar
tsubbu
Hukumar yan sanda a jihar nija ta kama wani magidanci Likita
Manu mai shekaru 40 wanda ya kashe mahaifiyar sa kan
zargin kashe mai diyar ta hanyar tsubbu.
Jaridar punch ta kawo rahoto cewa an kama Manu tare da
mahaifn sa Kwacha mai shekaru 80 wanda ya taimaka masa
wajen dukan mahaifiyar har numfashin ta ya dauke.
Labari ya nuna cewa manu ya hau mahaifiyar shi da duka bisa
ga zargin kashe mai diya ta hanyar tsubbu.
Shima mahaifin sa Kwacha ya taimaka mai wajen aikata laifin
wanda yayi sanadiyar mutuwar matarsa. An kama su ne bayan
karar da makwabta suka kai ga rundanar yan sanda.
yayin da yake bada amsar tambayoyi a ofishin yan sanda
mahaifin ya shaida cewa yarinyarb itace mutum na tara da
matarsa Kaiyo ta kashe ta hanyar tsubbu kuma ba wai yayi
niyan kashe ta ba, lamarin ya faru ne bayan ya nemi ya dan
zane ta da icce bisa ga abun da tayi da jikan sa wanda ya
fusatar dashi.
Da aka tambeyi shi ta yaya ya gano cewa mahaifiyar shi ta
kashe diyar shi Manu yace:
"Mun gano ta hanyar diyata Magajiya yayin da take jinyar wata
rashin lafiya. Tana ta kuka tare da rokon kakar ta Inne Kaiyo da
ta saki ruhin ta.
Muma mun roke ta amma taki amincewa. kuma ina sane cewa
mahaifiya ta mayya ce."
Jami'in hulda da jama'a na rundunar Asp Abigail Adaeze ta
tabbatar da lamarin kuma tace za'a gurfanar dasu gaban kotu
bayan an gama bincike akan su.
CLICK HERE TO GET MORE NEWS
NUT blasts Buhari over endorsement of El-Rufai’s sacking of 22,000 teachers
- NUT has faulted President Muhammadu Buhari’s
endorsement of Governor El-Rufai’s sacking of 22,000
teachers
- Governor El-Rufai of Kaduna state had sacked 22,000
teachers in the state over failure of competency test
- The union said that it would be unfair if President
Buhari had listened to the one-sided story and decided
to endorse sacking of the teachers by El-Rufai
The Nigeria Union of Teachers (NUT) has faulted
President Muhammadu Buhari for endorsing the
laying off of about 22,000 teachers in Kaduna
state.
New Telegraph report that the general secretary
of the NUT, Dr. Mike Eneh, said on Monday,
November 13, in Abuja that rather than layoff
teachers under the guise of having failed a
competency test, a retraining programme ought
to have been organized to boost the quality and
efficiency of the teachers in the state.
arewaupdates.com gathered that the Eneh said the
government of Kaduna state had no right
whatsoever to conduct any form of test for
teachers, as such was the mandate of the
Teachers Registration Council of Nigeria (TRCN).
He noted that the Governor of Kaduna state,
Mallam Nasir El-Rufai, had only ended up
embarrassing himself and the state, and have
proven beyond all reasonable doubt, the
educational imbalance between the north and
the south.
“It will be unfair if Mr. President listen to the one-sided
story and decide to sack the teachers. If I were Mr.
President, I could have called all parties involved including
the stakeholders, the NUT, the people that set the exams
and we dialogue to proffer solutions to know what to do,”
he said. Eneh who described the competency test and
alleged failure as a lame excuse to cut down cost
by reducing the workforce in the state disclosed
that the union was not resting on its oars, but
was joining forces with the Nigeria Labour
Congress (NLC) to address the situation.
“The supervisory department of Kaduna state education
department in the primary education from their Kaduna
state superb is dead. That is simply what it means
otherwise they were just conniving with the people to
collect government money and they were eating it.
“Our position is that El-Rufai and the government of
Kaduna state have decided to cut down on their workforce.
We have learnt that local government and civil servants are
on the line to take their own exams, if 22, 000 teachers can
fail, it then means that civil servants and the local
government workers who do not have the opportunity of
going to school will fail the exams and he will sack
everybody.
We are not laying low; we have several options
we are going to take. The NUT has the backing of
NLC, we are going to face him one on one.
Nobody is intimidating him all we are saying is
that as a governor he should give room for
dialogue.
“Even in governance we cannot clap for all the governors
and say that they are the best but to tell us that 21,000
teachers fail exams does not go down well with us. We are
disputing it, we are arguing it and we want to find out how
the 21,000 teachers failed. If we dialogue and we are
convinced what he did was real and that nobody was
cheated, we give up,” he added.
At the time of filing this report, the leadership of
the Nigeria Labour Congress was unavailable to
react, as they were in the middle of an intense
meeting deliberating on their next move.
Meanwhile, arewaupdates.com.ng had previously reported
that President Muhammadu Buhari backed the
plans by Governor Nasir El-Rufai to sack 22,000
Kaduna teachers under an educational reform
being undertaken by the Kaduna state
government.
A yaune Buhari ya goyi bayan sallamar malamai 22,000
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya goyi bayan sallamar
malamai kimanin 22,000 wadanda suka fadi jarrabawar da
gwamnatin jihar Kaduna ta yi musu.
13 Nuwamba 2017
Sunday, 12 November 2017
Labari da dumiduminsa-An gano diamond da nauyinsa ya kai karat 400 a Saliyo
Masu hakar ma'adinai a Saliyo sun hako wani diamond wanda
nauyinsa ya kai karat 476, kuma an ce shi ne diamond na 29
ma fi ya girma da aka gano.
Kawo yanzu dai kwararu basu tabbatar da darajar ko kuma
kudin diamond din ba.
Lamarin dai na zuwa ne bayan da aka gano wani daimaond da
nauyinsa ya fi karat 700, wanda shi ne diamon mafi girma da
aka gano a Saliyo a cikin rabin karni.
A watan gobe dai zaa ayi gwajonsa a birnin Newyork na
Amurka.
Shugaban hukumar ma'adinai ta kasar Saliyo, Sahar Wonday ya
ce diamond din da aka gano ya nuna cewa akwai albarkatun
kasa masu daraja a yankin Kono, inda a nan ne aka gano
dukannin daimond din su biyu.
Kasar na son tayi amfani da cinikin watan Disemba domin ta yi
kokarin kawar da abubuwan da suka faru a baya watau yakin
basasa da aka shafe shekara 11 ana yi wanda kasuwanci
diamond na cikin abubuwan da suka rika ruruta rikicin.
Must read - Policeman beats Nigerian soldier at ATM stand in Damaturu (photos) click to check out what happened
A Nigerian police officer has allegedly beaten up a
soldier in Yobe state
- The soldier was allegedly beaten up for trying to
jump the queue at an ATM stand in Damaturu
- It was gathered that the police officer tried to talk to
the officer but the two started to exchange words
when the fight suddenly began
A policeman in Yobe state has beaten up a
soldier who tried to skip the queue at an
Automated Teller Machine stand to withdraw
money.
According to reports, the soldier who was
dressed in his uniform came to the ATM stand to
withdraw without making an attempt to join the
long queue.
The people at the queue reportedly started to
protest when they realized what the soldier was trying to do.
It was gathered that the police officer confronted
and demanded that he should join the queue like
everyone else.
The fight suddenly began after the two men
started to exchange words with each other. The
policeman was said to have overpowered the
soldier in the fight.
According to Dailypost, they were separated
when a witness called the attention of the police
and military force in Damarutu.
It was reported that a senior military officer
came to pick up the soldier who was wounded to
the base for treatment.The police officer and other officers who were on
duty at the bank were allegedly taken for
interrogation by Mopol officers in Damarutu.
If any police officer misbehaves with you, call
any of these numbers - on www.lgvtube.blogspot.com
Source: www.lgvtube.blogspot.com
soldier in Yobe state
- The soldier was allegedly beaten up for trying to
jump the queue at an ATM stand in Damaturu
- It was gathered that the police officer tried to talk to
the officer but the two started to exchange words
when the fight suddenly began
A policeman in Yobe state has beaten up a
soldier who tried to skip the queue at an
Automated Teller Machine stand to withdraw
money.
According to reports, the soldier who was
dressed in his uniform came to the ATM stand to
withdraw without making an attempt to join the
long queue.
The people at the queue reportedly started to
protest when they realized what the soldier was trying to do.
and demanded that he should join the queue like
everyone else.
The fight suddenly began after the two men
started to exchange words with each other. The
policeman was said to have overpowered the
soldier in the fight.
According to Dailypost, they were separated
when a witness called the attention of the police
and military force in Damarutu.
It was reported that a senior military officer
came to pick up the soldier who was wounded to
the base for treatment.The police officer and other officers who were on
duty at the bank were allegedly taken for
interrogation by Mopol officers in Damarutu.
If any police officer misbehaves with you, call
any of these numbers - on www.lgvtube.blogspot.com
Source: www.lgvtube.blogspot.com
Saturday, 11 November 2017
An Kama Wani kafurin Boka Da Kasusuwan Mutane
WASHINGTON, DC — Rundunar ‘yan Sandan jihar Abia ta
damke wani Boka, bayan ta ta same shi da wasu bangarorin
mutane da kasusuwa.
Kwamishinan ‘yan Sandan jihar Mr. Leye Oyebade, ne ya
shedawa manema labarai a garin Umuahia, cewa mutumin da
aka damke, ya kasa baiwa hukumomin wani dalili mai
gamsarwa a lokacin da akayi mashi tambayoyi.
Yana mai cewa kwarangwal din kai da wasu kasusuwan da
aka samu an zargin na irin mutanen da ake kashewa ne.
Wanda ake zargi ya musanta zargin yana mai cewa yayi
gadon sune a wurin wani kawun sa wanda shima boka ne
kafin rasuwarsa.
Yace mutanan su ne suka kai karansa wajen ‘yan Sanda
domin yana amfani da kasusuwan wajen yin siddabaru.
Ya kara da cewa duk wanda ya taba sai mazakutan say a
bace idan har kasusuwan na tare dashi.
Shi dai wannan Boka wanda kuma magini ne ya ce ‘yan
Sandan sun yi nasarar damke shine saboda asirin da yake
amfani dashi yayi balaguro, da cewa kama shi da akayi ba
daidai bane saboda haka ya bukaci da a sake shi.
Yadda giwar ruwa ke cin kwari miliyan 40 a rana ikon Allah.
Tsananin son cin abinci da matsananciyar yunwa da galabaita.
Daukacinmu akwai ranakun da mukan yi fama da yunwa,
amma ko yunwarka ta kai ga bukatar cin ton hudu na halittar
ruwa?
Batu na gaskiya, shudin hamshakin kifi (the blue whale) giwar
ruwa ita ce babbar dabbar da ta fi kowace girma a duniya, inda
ta sha gaban komai a zakuwar son cin abinci.
A kullum wannan kasurgumar dabba tana lakume kananan
kwari miliyan 40, wadanda ake yi wa lakabi da kananan kifaye
Sai dai akwai sauran dabbobi da ke cin abinci ba na wasa ba,
ta yadda wasunsu za su ba ka mamaki.
Tamkar hamshakin shudin kifi, wannan katafariyar dabbar
doron kasa tana cin abinci daidai da dundumemen jikinta.
A cewar kwararrun masana kan giwar Afirka, Norman Owen-
Smith na Jami'ar Witwatersrand da ke Johannesburg a Afirka
ta Kudu, inda namijinta ke lakume kaso guda cikin 100 na
nauyinta a kan busasshen tundurkin kasa a ko wacce rana,
yayin da ta-macen da ke shayarwa ke cin kashi 1.5 cikin 100
don su ci gaba da rayuwa.
Panda na cin abincin da nauyinsa ya kai kilo 12.5 na
kwangwala ko wacce rana.
Namijin yana da nauyin ton 6, don haka abin da yake ci
nauyinsa ya kai kilo 60 na busasshen abinci ba tare da an hada
da yawan ruwan da ta kwankwada ba, al'amarin da ka iya
nunkawa da rubi hudu.
Hamshakan dabbobi masu shayarwa kan shafe tsawon rana
wajen kai-kawon cin korayen tsirran da ke ba su kuzarin
rayuwa. Sukan iya shafe sa'o'i 18 suna cin abinci a rana,
gwargwadon abin da ya samu.
Haka kuma hamshakiyar yanyawar Sin (Panda) kan shafe sa'o'i
14 tana gwagwiyar kwangwala.
Masu bincike sun yi nuni da cewa wanan abincin bai cika
kosar da dabbobin ba, wadanda tsarrin sarrafa abincinsu na
iya sarrafa ko wanne irin nau'in abinci, wanda da sarrafa
dimbin tsirrai ba.
Wannan ke nuni da dalilin da ya sanya yanyawar Panda ke cin
dimbin abincin da nauyinsa ya kai kilo 12.5 na kwangwala a ko
wacce rana don samun isasshen abincin da suke bukata, kuma
shi ne hujja da ke nuni da kimar kashinsu.
Daukacin maciyan tsirrai kan shafe tsawon lokaci suna bibiyar
dimbin gayayyaki da itatuwa don samun isasshen abincin da
zai ba su kuzari, yayin maciyan nama kan mayar da hankali kan
kayan makwalashe (abincin da ake dafawa cikin gaugawa).
Brock Fenton na Jami'ar Western da ke Canada ya ce adadin
an "zuzuta shi," sakamakon rudanin da aka samu a tsakanin
nau'ukan binciken biyu mabambanta da aka gudanar kan
nau'ukan jemage a shekarun 1950.
Nau'ukan jemagen Japan kan shirya shirin cin abinci na gaba
kafin ma ya lakume wanda ke gabansa.
Fenton ya ce daya daga binciken da aka gudanar ya yi nazari
ne kana bin da ke cikin jemage mai launuka uku bayan ya
gama cin abinci, yayin da dayan kuwa ya bi kadin nau'ukan
jemage kananan masu launin kasa-kasa a dakin binciken kan
yadda yake kama sauraye da kudajen da ke zarya kan 'ya'yan
itace.
Babu daya daga cikin binciken da ya bayar da adadin na
gaskiya kan yawan kwarin da karamin jemage mai launin kasa-
kasa ke lakumewa a daji.
Kuma karamin jemage mai launin kasa-kasa na cin dimbinci ba
wai sauraye kadai ba: sun ma fi son abubuwan masu girma,
kamar tsutsotsi, a duk lokacin da suka samu damar kama su.
Wani bincike da aka gudanar kan jemagu a kasar Canada ya yi
nuni da cewa sauraye wani yanki ne kadan daga abincinsu.
Don haka ta yiwu fadadawa aka yi cewa suna iya lakume
sauro a ko wacce dakika 3.6.
Sai dai akwai hujjar da ke nuni da cewa ire-iren jemagu sukan
kara kaimin farautar abincinsu doin samun gwargwadon abin
da ya wadata da suke ci.
A shekarar 2016 bincike ya nuna cewa Jemagun Japan kan
shirya cin abinci na gaba kafin ma su lakume wand ake
gabansu.
Sabanin yadda ake ganin tashinsu, jemagun kan tsara
shawaginsu bisa la'akari da irin abin da za su iya sura a hanya.
Akwai sauran kananan kasa-kasan dabbobi masu shayarwa
wadanda ke cin abinci babu kakkautawa: nau'ukan jabar daji
(the shrews).
A kalla ko wacce tsiryar Amurka hummingbird na lakume
sukarin da ya kai rabin nauyinta a ko wacce rana.
Jabar dawan da aka sani dole ta ci abin da ya yi daidai
nauyinta da kashi 80 zuwa 90 cikin 100 a tsakanin sa'o'i 2 zuwa
3.
Karamar jabar dawa, wadda ta kai rabin girman 'yar uwarta
tana cin kashi 125 cikin 100 na abincin da ya kai nauyin jikinta
a kowace rana.
Irin wadannan dabbobi masu shayarwa suna da saurin sarrafa
abinci, al'amarin da ke nuni da cewa nan take zai narke ya ba
su kuzari cikin hanzari.
Don haka sai sun ci abinci akai-akai dibge da abinci mai kara
lafiya na protein da dabbobi masu kasha ke ci ko yunwa ta
halaka su.
Duk wata tattaunawa kan sarrafa abinci to za ta bi kadin tsiryar
Amuyrka (hummingbirds).
Wadannan halittu masu tashin ban mamaki sun fi shan zakin
sukari don samun kuzarin tashi. Sukan bubbuka fuka-fuklinsu
sau 50 a kowace dakika, irin wadannan tsuntsaye sun fi saurin
sarrafa abinci a jerin dabbobi masu kashi.
Ta yiwu ka ji labarin cewa akalla tysiryar Amurka na lakume
zakin sukari da ya kai kimar rabin nauyin jikinta a kowace rana,
inda take cin abinci bayar kowane minti 15 a furannin kallo.
Akan sarrafa dimbin sinadarin kuzari da ke tare don bunkasa
karamin dan tayi zuwa tsutsar siliki.
"Yawan zakin furen kallo da tsiryar Amurka ke lakumewa na iya
bambanta," a cewar Adam Hadley, ja-gaban masu binciken
tsiryar Amurka (hummingbird) a Jami'ar Jihar Oregon.
"Musamman tunda suna da mabambanta girman jiki, wanda ya
kama daga giram 2.5 na kudan tsiryar Amurka (bee
hummingbird) zuwa babbar tsiryar (giant hummingbird)."
Yayin da manya ke kwankwadar dimbin zakin furanni, suna
sarayar da makamashin kuzarinsu ne a hankali fiye da kananan
tsuntsaye. Wannan na nuni da cewa, in an kwatanta, kananan
halittu sun yi fama da matsananciyar yunwa.
Hadley ya ce tsuntsaye na adana makamashi har zuwa lokacin
da suka bukaci amfani da shi. "Abin sha'awar shi ne yadda
suke adana abin da ya kai kashi 17 cikin 100 na nauyin jikinsu
na maiko, ta yadda za ta kasance kowace tsiryar amurka za ta
yi amfani da 30lb a rana guda."
Sauran nau'ukan halittu na nuni da cin abincin ban mamaki a
wani yanayin lokaci na rayuwarsu. Alal misali, akwai bukatar
dimbin makamashin kuzari don bunkasar dan-tayi zuwa
tsutsar siliki.
Kwaron tsutsar siliki (The Polyphemus moth) an yi masa lakabi
ne da sunan gwarazan Girkawa da Homer ya bijiro da su a
labaran ban mamaki, saboda a kowane fufffike yana da alamar
kwayar ido.
Sai dai daukacin halitta mai cin mutum da tsutsa mai lakume
tsirrai abu guda ne wajen zakuwar son cin abinci da yawa.
Don mu kamo tsutsa, sai mun rika cin abincin da nauyinsa ya
kai laba 50 zuwa 200 na latas a kowace rana.
Kamar yadda Kundin shahararrun al'amuran duniya Guinness
ya tattara cewa, kwaron tsutsa irin "caterpillar" na cin abincin
da nauyinsa ya rubanya na jikinta sau 86,000 a kwanaki 56.
Amma Andrei Soirakov jagoran masu tattara bayanai a gidan
kayan tarihin albarkatun kasa na Florida cewa ya yi, akwai
tababa kan adadi.
Wanan kawai tamkar ka auna abin da mutum ke ci ne tsawon
rayuwar yarintarsa, sannan ka kwatanta shi da nauyinsu a
lokacin da suke kamar jariri sabuwar haihuwa.
Sourakov ya ce aikin da aka gudanar kwanan nan a Jami'ar
Florida ya gano cewa kwaron luna, wanda yake kwatankwacin
girin irin wadannan halittu, kawai suna cin abin da ya kai rabi
ko biyu bisa uku na nauyin jikinsu a ko wacce rana.
"Har yanzu dai lamarin da kayatarwa," inji Sourakov. "doin su yi
daidai da kwaron tsitsar 'caterpillar' to sai mun ci laba 50 zuwa
200 na latas kowace rana."
Karara yake, a cewar Eric Carle yunwar kwaron tsutsar
caterpillar ta shahara ba kai makurar da ake nuni da ita ba.
Dabba ta karshe da muke bin kadin tsananin yunwarta a duniya
ba lallai su kasance mashahuran abubuwan da ake nuni da su
a littattafan labarai na yara.
Ko da yake yanayin cina bincinsu na musamman an tattaro shi
ne don ceton rayuwar mutane, inda aka siffanta su da dodanni
masu ban tsoro.
Ana amfani da tsutsotsi masu zukar jini don warkar da gyambo
karnoni da dama. Sai dai mafi yawan nau'ukan tsutsotsin 700
suna lakume halittu marasa kasha, wato tamkar yadda tsutsar
tsibirin Borneo mai ban tsoro ke farauta.
Jagoran nazarin tsutsa mai shan jini ya taba ganin
"hamshakiyar" tsutsar da aka tsareta, inda take samun abinci
ba tare da sun cutar da kowa ba.
"Manyan tsitsotsin da na taba gani samfuran manyuan
tsutsotsin dajin Amazon ne da ake yi wa lakabi da
'Haementeria ghilianii' da bajimin tsutsar Asiya mai lakabin
Hirudinaria manillensis," in ji Siddall.
Ya kara da cewa, "Wadannan daidaikun tsutsotsin babu
tantama su suka fi zukar jini."
Sai dai a daji, damar samu ke da tasirin kan son cin
abinci.Tsutsotsin kungurmin daji sun yi kankanta da farauta,
don haka suke jiran abin da za su iya lakumewa ya kawo
kansa.
Saboda tsawon jiran da suke yi, ba abin mamaki ba ne su yi ta
hadama su cika cikinsu da zarar dama ta samu sai su ci har
girmansu ya rubanya nauyin jikinsu sau bakwai bayan sun
kwankwadi jini.
Wannan shi ne isasshen abin da kowane zai lakume.
Shiga rukunin mutum fiye da miliyan shida da ke sha'awar
shirin BBC kan doron kasa, ta hanyar latsa maballin kauna a
shafinmu na Facebook ko a bniyo mu a shafinmu na Twitter
da Instagram.
Ba za mu manta da gwamnatin Buhari ba —inji yan Shi'a
Wani mabiyin mazhabar Shi'a a Najeriya da aka fi sani da
Islamic Movement of Nigeria, IMN karkashin jagorancin
Sheikh Ibrahim Elzakzaky, ya ce ba za su taba mantawa da
'rashin adalcin' da shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya
yi musu ba dangane da al'amarin da ya faru tsakaninsu da
sojoji a Zariya.
Ahmad Bawa Jalam ya ce da shi da sauran mabiya jagoran
IMN ba za su gushe ba face suna addu'ar neman sakayya daga
Ubangiji.
A ranar 10 ga watan Disambar 2015 ne dai sojojin suka yi
zargin almajiran Sheikh Zakzaky da tsare wa babban hafsan
sojin kasar, Janar Yusuf Tukur Buratai hanya da kuma kokarin
hallaka shi.
Bayan nan ne kuma sojojin suka far wa gidan shugaban na
IMN, sheikh Elzakzaky bisa dalilan bayanan sirri da suka samu
da ke nuna mabiya mazhabar ta Shi'a na shirin daukar matakin
kai hare-hare, al'amarin da ya janyo kisan mabiya mazhabar da
dama sannan kuma aka kama shugaban kungiyar da har yanzu
ke tsare a hannun gwamnati.
Sojojin dai sun ce mutum takwas ne suka mutu sakamakon
samamen, a inda bakwai daga ciki 'yan Shi'a ne sannan kuma
guda daya soja.
Sai dai kungiyar IMN ta musanta alkaluman a inda da farko ta
ce an kashe mata 'ya'ya fiye da 500 sannan kuma daga bisani
ta ce an kashe kusan mutum dubu daya.
To amma wani kwamitin bin bahasin hakikanin abin da ya faru
da gwamnatin jihar Kaduna ta kafa ya gano abubuwa da dama
da suka hada da kisa da binne mabiya mazhabar ta Shi'a 347 a
asirce.
Wannan ne ya sa mabiya jagoran na IMN, kamar Ahmad Bawa
Jalam ke ganin shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ba zai
taba kubuta daga zarginsu ba.
Ku saurari hirar na yi da Ahmad Jalam:
Matsayin kotu kan Elzakzaky
A watan Disamban 2016, wata babbar kotu a Abuja ta nemi
gwamnati ta saki Elzakzaky da matarsa tare da biyan sa diyya
sannan kuma a gina masa gida, a duk garin da yake so a
arewacin kasar, duk a cikin kwanaki 45.
To amma har yanzu gwamnati na ci gaba da tsare Elzakzakyn
bisa wasu dalilai da ministan Shari'ar kasar, Abubakar Malami,
ya ce ta dogara da su.
"Idan irin wannan ya faru a kan rinjayar da bukatar al'umma
fiye da ta mutum guda," in ji Malami.
Ya kara da cewa "Idan an bayar da oda ko kuma hukunci, ya
zama an daukaka kara akwai bukata wadda doka ta amince da
ita na ainihin wanda bai gamsu ba ya nemi dakatar da zartar
da hukunci."
Ga dai yadda hirar tasa ta kasance da Editanmu na Abuja,
Naziru Mika'ilu:
Da man dai mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo
ya ce ba za su saki jagoran IMN ba duk da kotu ta ce a sake
shi, bisa dalilan shari'a da na tsaro
Me lauyoyi ke cewa?
Masana shari'a da dama dai na ganin ya kamata gwamnati ta
yi adalci sannan kuma ta girmama kundin tsarin mulki sannan
su kuma mabiya Shi'a su yi hakuri su bi doka tunda dai
gwamnati ta ce za ta kalubalanci hukuncin kotu.
Barista Sunusi Musa, wani lauya mai zaman kansa a Najeriya
ya ce, "Tunda dai gwamnati ta ce za ta daukaka kara sannan
kuma ta gindaya batun tsaro, lallai ya kamata mabiya Shi'a su
kwantar da hankalinsu su ci gaba da neman hakkinsu ta hanyar
tsarin dokar kasa."
Sai dai kuma Barista Sunusi ya kara da cewa, "Ni a ra'ayina zan
so a ce an saki Elzakzaky domin bin umarnin kotu."
"Wani lokacin akwai bukatar gyara a harkar shari'ar Najeriya
saboda bai kamata a ce kotu ta bayar da umarni ba amma a ki
bin sa," in ji Sunusi Musa.
Matsayin kungiyoyin 'yancin danadamg
Kungiyoyi masu fafutukar kare 'yancin dan adam a Najeriya da
ketare kamar Amnesty International sun fito balo-balo suna
zargin gwamnatin Najeriya da rashin mutunta 'yancin mabiya
Shi'a.
Da man dai kungiyar Amnesty International ce ta fara fadin
cewa ta gano wurin da aka binne 'yan Shi'ar da aka kashe a
Zariya, a asirce.
A har ko yaushe kuma kungiyar tana ci gaba da sukar ci gaba
da tsare shugaban IMN, Ibrahim Elzakzaky ba tare da gurfanar
da shi a gaban kuliya ba domin ya fuskanci hukunci.
A baya-bayan nan ne kuma aka kara samun wasu kungiyoyin
masu rajin kare hakkin dan adam da ke cikin Najeriya kamar
Concerned Citezens suka yi ta gudanar da zanga-zanga iri-iri
tare da mabiya Shi'a domin neman a saki Elzakzaky.
Zanga-zangar neman sakin Elzakzaky
Tun dai kama da tsare jagoransu a watan Disambar 2015,
mabiya mazhabar Shi'a suke ta fama gudanar da taruka da
zanga-zanga iri-iri domin a bi musu kadinsu da kuma sakin
shugabansu da ma sauran 'yan kungiyar da suka yi zargin suna
tsare.
Ma fi yawancin lokuta dai 'yan Shi'ar na haduwa da fushin
jami'an tsaro a inda suke tarwatsa su bisa dalilin cewa 'yan
Shi'ar ba sa neman izinin hukuma.
Sannan kuma suna shiga hakkin mutane ta hanyar tsare
hanyoyi ga matafiya.
To amma Barista Sunusi Musa ya ce, "Duk da cewa ko wane
dan Najeriya yana da hakkin gudanar da taro ko nuna
damuwarsa ga wani abu idan dai har ba zai karya doka ba ko
kuma ya take hakkin wani, ya kamata 'yan Shi'a su rinka sanar
da jami'an tsaro kafin gudanar da zanga-zanga domin jami'an
tsaron su ba su kariya."
Sai dai mai magana da yawun IMN, Ibrahim Musa ya ce, "Babu
inda aka ce sai ka shaida wa jami'an tsaro za ka gudanar da
taro ko zanga-zanga."
Ya kuma ce, "Batun a ce muna tare hanya wannan kuma ba
haka ba ne kawai dai makiyanmu ne suke fada domin samun
abin da za su soke mu da shi."
A baya dai shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya yi kira
ga jami'an tsaron kasar da su yi taka-tsan-tsan wajen dakile
ayyukan 'yan Shi'a.
Gwamnatin jihar Kaduna da IMN
Gwamnatin jihar Kaduna ta kafa wani kwamitin bin bahasin
hakikanin abun da ya faru tsakanin sojoji da 'yan Shi'a a Zariya
kasancewar garin na karkashin jihar.
Kwamitin kuma ya gano abubuwa da dama da suka hada da
kisa da binne mabiya mazhabar Shi'a 347 a wasu wawaka-
wawakan ramuka na bai daya.
Sannan kuma ya bayar da shawarwari masu yawa kan yadda
za a guji afkuwar irin rikicin a gaba.
Shawarwarin dai sun hada da hukunta jami'an tsaron da suka
aiwatar da kisan 'yan Shi'a a Zariyar da haramta kungiyar 'yan
uwa musulmi ta IMN tare kuma da hukunta shugabanta,
Elzakzaky.
Tuni kuma gwamnatin jihar ta haramta gudanar da ayyukan
kungiyar sannan ta sha alwashin hukunta Elzakzaky, kamar
yadda a baya-bayan nan gwamna Nasir Elrufa'I ya shaida wa
wata kafar talbijin a Najeriyar cewa, "Muna jira gwamnatin
tarayya ta miko mana Elzakzaky domin mu samu mu gurfanar
da shi a gaban kotu."
To sai dai har kawo yanzu gwamnatin ba ta aiwatar da
shawarar hukunta sojojin da suka kashe 'yan Shi'ar ba kamar
yadda kwamitin ya bukata.
Hakan ne ya sa lauyan Elzakzaky, Femi Falana ya nemi da
gwamnatin ta jihar Kaduna da hukunta jami'an tsaron.
A wata sanarwa da ya aike wa da BBC, Mista Falana ya ce,
"Dole ne a hukunta jami'an tsaron da suke da hannu a kisan
Zariya, idan kuma ba haka ba to za su gurfanar da su a gaban
kotun hukunta manyan laifuka ta duniya wato ICC."
Ya ya za a warware rikicin Shi'a da gwamnati?
Masana a fannin shari'a kamar Barista Sunusi Musa na ganin
za a iya shawo kan rikicin gwamnati da 'yan Shi'a ta hanya
biyu:
Sulhu
Shari'a
Dangane da sulhu, Barista Sunusi Musa ya ce, "Gwamnati za ta
iya zama da Elzakzaky da mabiyansa a tattauna, kamar yadda
aka yi da tsagerun Naija Delta. Idan abin ya kama a bayar da
diyya sai gwamnati ta bayar tun da mun ga yadda aka yi kan
kisan sirikin shugaban Boko Haram, Muhammadu Yusuf, a inda
gwamnatin jihar Borno ta bayar da diyyar naira miliyan dari."
To amma Sunusi ya kara da cewa, "Ita ma gwamnati za ta iya
zayyana wa jagoran Shi'ar irin bukatunta sannan dole ne
Elzakzaky da mutanensa su martaba dokar kasa."
Abin kuma da ya shafi shari'a, Barista Sunusi ya ce, "Idan har
sulhun bai yiwu ba sai a je ga matakin gurfanarwa a gaban
kotu, idan kotu ta same shi da laifi ta hukunta shi, idan kuma
ba shi da laifi ta sake shi."
Illar rikicin Shi'a da gwamnati ga tsaron kasa
Masana harkar tsaro a Najeriya sun ce idan dai har ba a bi
matakan da masana shari'a suka zayyana ba wajen warware
takaddamar Shi'a da gwamnati, to fa kasar za ta fada cikin
wani hali.
Dr. Kabiru Adamu, wani masanin tsaro ne a Najeriya kuma ya
zayyana matsalolin da Najeriya za ta iya fadawa idan har rikicin
Shi'a da gwamnati ya ci gaba da wakana:
"Idan Elzakzaky ya mutu a hannun gwamnati, babu
makawa 'yan Shi'a za su ce gwamnati ce ta kashe shi
saboda haka Allah kadai ya san abun da zai faru."
"Rashin magance wannan rikici zai iya janyo mummunan
rikicin banbancin akida tsakanin Shi'a da Sunna kamar
yadda ake gani a wasu kasashen gabas ta tsakiya."
"Al'amarin zai iya sanya wasu kungiyoyin addini su fara
shirin kare kai, kafin gwamnati ta zo kansu su ma."
Abin da 'yan Shi'a ke bukata
Mai magana da yawun Islamic Movement of Nigeria, Ibrahim
Musa ya shaida wa BBC cewa, "Muna da bukatu da yawa
amma dai babbar bukatarmu yanzu haka ita ce a saki
jagoranmu, Sheikh Ibrahim Zakzaky da matarsa da sauran 'yan
uwan da ake tsare da su", a inda ya ci gaba da fadin, "alabashi
idan aka sake shi to sauran bukatun shi ya san yadda za a yi
da su."
Sharhi
Masana a fannin shari'a da tsaro dai sun daki jaki da kuma
taiki kan rikici tsakanin 'yan shi'a da gwamnati.
Yayin da Dr Kabiru Adamu ya ke ganin, "Najeriya ta yi amfani
da karfi fiye da kima wajen dakile ayyukan tsirarun mabiya
Shi'a", shi kuwa Barista Sunusi Musa ya ce, "Dole ne 'yan Shi'a
su san cewa bin doka dole ne a matsayinsu na 'yan Najeriya."
Sai dai kuma Barista Sunusi ya kara da cewa, "Gwamnatin
Najeriya ita ma ya kamata ta san cewa 'yan Shi'a suna da
'yancin yin addinin da suka ga dama."
A yanzu dai a iya cewa, al'ummar kasar ta zura ido ne don
ganin ya ya za ta kaya tsakanin gwamnati da kungiyar IMN kan
batun sakin jagoran nasu da sauran 'yan uwansu da aka kama,
musamman a daidai wannan lokaci da Shugaba BUhari ya cika
shekara biyu a kan mulkin kasar.
Wanda ya fallasa dalolin da EFCC ta gano a Lagos ya 'zama miloniya' IKON ALLAH!!!.
Hukumar EFCC da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin
Najeriya ta'annati ta ce mutumin da ya fallasa kudin da aka
gano a wani gida a unguwar Ikoyi da ke jihar Legas "ya zama
miloniya."
Shugaban riko na hukumar, Ibrahim Magu, ne ya tabbatar da
haka a wani taro a birnin Vienna na kasar Australiya, in ji
sanarwar da mai magana da yawun hukumar Wilson Uwujaren,
ya fitar.
Uwujaren ya tabbatar wa BBC cewa hukumar ta bai wa wanda
ya fallasa boye wadansu makudan kudade a wannan gida,
amman ya ki ya bayyana nawa aka bai wa mutumin.
A shekarar da ta wuce ministar kudin Najeriya, Kemi Adeosun,
ta bayyana shirin gwamnatin kasar na bayar da tukuicin kashi
biyar cikin 100 ga duk wanda ya fallasa "haramtaccen kudin"
da ake zargin na sata ne.
Idan aka yi la'akari da cewa kudin da aka samu a gidan na
Legas a farkon shekarar nan ya kai naira biliyan 13, za a iya
cewa wanda ya kwaramata bayanin kudaden zai samu kimanin
naira miliyan 650 (kashi 5 cikin 100 na kudin da aka samu a
cikin wani bene a Legas).
Bayan hukumar EFCC ta yi wawan kamun ne dai aka gano
cewa kudaden suna da alaka da tsohon shugaban hukumar
leken asirin Najeriya ta NIA, Ayo Oke.
Wannan ya sa shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya sa
aka dakatar da Mista Oke daga farko, kuma ya kore shi daga
baya.
Subscribe to:
Posts (Atom)